Gulma da Tsegumi a Tunanin Bahaushe: Nazari Daga Habarcen Hausa

    Tsakure

    Al’ummar Hausawa, al’umma ce da take da hanyoyi mabambanta na tantance abubuwa masu ɗimbin yawa, waɗanda suke abin koyi da kuma munana waɗanda Hausawa suke ɗaukar su a matsayin abin ƙyama. Gulma da tsegumi suna ɗaya daga cikin munanan halaye da ɗabi’un da Hausawa sukan yi hani da aikata su. Gulma da tsegumi ɗabi’u ne marasa kyau da suka daɗe a cikin al’umma. Kamar yadda ba a san ranar da aka fare su ba, haka kuma ba a san ranar barin su ba. Duk da an san ƙarshen mai yin su shi ne jin kunya. Wannan takardar ta kalli ɗabi’ar daga gulma da tsegumi ne daga adabin baka na habarce da tatsuniya ta hanyar fito da gulma da tsegumin da kuma matsayinsu a al’adun Hausawa da ma dalilan yin gulma da tsegumin. Gulma da tsegumi abubuwa biyu ne masu makusanciyar ma’ana, amma da an ambaci gulma da abu mara kyau aka fi danganta shi. Shi kuwa tsegumi ba lallai ba ne ya zama abu mara kyau. Ana iya tsegunta wani alheri ga wani kamar yadda aka ga tsuntsuwa ta je ta tsegunta wa sarki labarin narkewar Ta-kitse.Wannan bincike ya gano dalilan da yake sanyawa ana gulma ko tsegumi da suka haɗa da: Hassada wato burin wani ya rasa wani abin da yake da shi da ƙyashi da kishi da son faɗar albarkacin baki. Kamar a tatsuniyar ta-kitse, a lokacin da gizo ya kai tsegumin cewa akwai wani tirkekken bajimin sa a gidan tsohuwa aka kuma je aka raba ta da wannan bajimin san. Haka kuma ya sake komawa ya sanya aka ɗauko wannan yarinyar a wurinta. A kuma labarin Shaihu Umar an ga yadda aka yi wa Makau hassada aka kai gulmarsa aka sa ya rasa komai har sai da aka kore shi a gari.

    DOI: 10.36349/zamijoh.2023.v02i02.013

    Download the article:

    author/ Muhammad Rabiu Tahir & Nura Lawal

    journal/Zamfara IJOH Vol. 2, Issue 2

    Pages