Tsakure: Taken wannan
maƙalar shi ne “Yanayin Korona a Idon Al’umma: Tsokaci Daga Bakin Marubuta
Waƙoƙin Hausa”. An shirya wannan maƙalar ne domin duba yadda wasu marubuta
waƙoƙin Hausa suka fito da yadda al’umma suke kallon annobar Korona a cikin
waƙoƙinsu. Annobar Korona sabuwar cuta ce da Hausawa ba su san ta ba kafin
watan Disamba 2019, inda ta bayyana a birnin Wuhan na ƙasar Sin, ta yaɗu a
sassan duniya duka. Kasancewar waƙa wani nau’in adabi ne mai tafiya daidai da
zamani ya sa aka samu wanzuwar wasu rubutattun waƙoƙin Hausa na Korona.
Hanyoyin da aka bi wajen gudanar da binciken sun haɗa da tattaro rubutattun
waƙoƙin Hausa da aka yi a kan annobar Korona, aka tsettsefe su da
karance-karance a ɗakunan karatu na jami’o’i da tattaunawa da masana a harkar adabi
da wasu marubuta waƙoƙin da kuma likitoci. Ra’in Tarihanci (Historicism Theory)
ne ya jagoranci binciken domin samun ingantaccen sakamako. A ƙarshe maƙalar ta
fito da gudummuwar da marubuta waƙoƙin Hausa suka bayar wajen bayyana yadda
al’umma suke kallon annobar Korona kama daga Sarakuna da malamai da talakawa da
kuma hukuma..
Fitilun Kalmomi: Annoba, Korona, Al’umma, Marubuta da Waƙoƙin Hausa
DOI: 10.36349/zamijoh.2026.v04i02.004
author/Bashir A. S., Bunza U. A. & Abba M. M.
journal/Zamfara IJOH Vol. 4, Issue 2


