Tsakure: Wannan muƙala ta tattauna sosai a kan wasu zihafai ne guda biyu da manazarta arulin rubutattun waƙoƙin Hausa suka ce ana karo da su a duk lokacin da ake auna karin waƙa. Takardar ta binciko yadda waɗannan zihafai suke da dangantakar da ke tsakaninsu da kuma irin rawar da suke takawa. An yi wannan aiki ne ta hanyar duba ƙafafuwa biyu da zihafan ke kamawa da kuma dangantakar da waɗannan ƙafafuwa ke da ita da junansu. Daga ƙarshe wannan nazari ya gano cewa zihafi Asbi da zihafi ilmaari tamkar Ɗanjuma ne da Ɗanjummai a cikin ra’in da aka ɗora aikin a kai wato Khalili.
DOI: 10.36349/zamijoh.2026.v04i02.005
author/Abubakar Sarki Muhammad
journal/Zamfara IJOH Vol. 4, Issue 2


